Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Ramadaniyyat (1440H) *[15]*

*Musulunci Cikakken Addini Ne* Allah yana cewa: (A yau na cika muku addininku, kuma na cika muku ni’imata, kuma na yardar muku Musulunci ya zamo shi ne addininku.) [Al-Ma'idah, aya ta 3].
Wannan aya ce da a ka saukar wa Manzon Allah (SAW) a ranar juma'a a filin Arfa a lokackin hajjinsa ta karshe. Wannan ayar ta tattaro abubuwa masu matukar muhimmanci a rayuwar Musulmi, domin tana dora su a kan mikakkiyar hanyar fahimatar addinin Musulunci. Cikin abubuwan da ayar ta kunsa akwai:

1. Addinin Musulunci ya cika tun lokacin da wannan ayar ta sauka. Duk abin da bai zama addini ba kafin saukar da wannan ayar, to ba zai taba zama addini ba bayan saukarta. Don haka duk wata bidi’a a addini bata ce, aiki da ita yana cin karo da wannan ayar. Shi ya sa Imamu Malik (RH) yake cewa: “Duk wanda ya kirkiri wani sabon abu a wannan addini, wanda magabatan wannan al’umma ba su san shi ba, to wannan yana ganin Annabi (SAW) ya ci amanar manzanci, domin Allah (SWT) yana cewa: “....A yau ne na cika muku addininku, kuma na cika muku ni’imata, kuma na yardar muku Musulunci ya zamo addininku.” To duk abin da ba zai zama addini a waccan rana ba, to a yau ma ba zai tava zama addini ba.” [Ibn Hazm, Al-Ihkam, juzu’i na 6, shafi na 58 da As-Shatibi, Al-I’itisam, juzu’i na daya shafi na 494].

2. Shari’ar Allah wani dunkulallen tsari ne wanda bai yiwuwa a yi masa gunduwa-gunduwa, a yarda da wani bangare, a yi watsi da wani; dole ne a yarda da shi a dunkulensa, musamman abin da ya shafi akida da ibada da mu’amala ta zamantakewar mutum da iyalinsa ko ta al’umma ko ta kasa da kasa. Duk wadannan abubuwa a dunkule su ake cewa ‘addini’, su ne kuma abin da Allah ya ce ya cika shi, kuma shi ne ni’imar da ya ce ya cika ta. Wadannan abubuwa a jumlace su ne tsarin rayuwa wadda Allah ya yarje wa muminai su rayu a kanta.

3. Musulunci shi ne mafi girman ni’imar da Allah (SWT) ya yi wa wannan al’umma. Duk wanda ya saki wannan addini na Musulunci, ko ya ki karbar sa, to ya haramta wa kansa rayuwa cikin ni’ima, ya zabi rayuwar musifa da wulakanci da kunci a duniya da lahira.

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...