Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadaniyyat

 (1440H) *[14]*
*Saukin Kai A Rayuwar Manzon Allah (SAW)*

1. Manzon Allah (SAW) mutum ne mai matukar saukin kai da tawalu'u ga kowa. Babu wanda ya taba tuhumar sa da girman kai har ma daga cikin manyan makiyansa na farko wadanda suka yi ta neman hanyar da za su bata shi a idon duniya, amma duk da haka ba wani daga cikinsu da ya yi tsaurin ido ya tuhume shi da girman kai.

2. Manzon Allah (SAW) ya kasance lahira kadai yake hangowa da zuciyarsa, amma duniya sam ba ta gabansa, don haka ya kasance bawan Allah na gaskiya, mai saukin kai ga muminai. Yakan dade a tsaye tare da tsohuwa mai bukatar zantawa da shi. Yakan je ya dubo marar lafiya. Yakan kuma tausaya wa mai rauni, ya taimaka wa mabukaci. Yana wasa da kananan yara, yana tsokanar iyalansa, yana cin abinci tare da sahabbansa. Yakan zauna a kan dandamalin kasa, har ma yakan yi barci a kanta idan ya bukaci haka, ko kuma ya kwanta a kan kungurumin tabarma wadda babu shimfida a kanta. Shuhura da neman suna ba sa gabansa, tunaninsa koyaushe shi ne neman yardar Allah (SAW).

3. Yana cewa: "Ni bawa ne kawai, ina cin abinci kamar yadda bawa yake ci, ina zama kamar yadda bawa yake zama".[Al-Baghawi# 2839].

4. Yayin da wani ya gan shi sai kwarjininsa ya cika masa ido da zuciya, har jikinsa ya fara bari, sai Manzon Allah (SAW) ya shiga lallashinsa da kwantar masa da hankali, yana fada masa cewa: "Kwantar da hankalinka, ni dan wata mace ce a Makka da take cin kilishi". [Ibn Majah# 3312].

5. Ya ki jinin ya ji ana wuce iyaka wajen yabonsa, don haka yake tsawatarwa yana cewa: "Kada ku wuce iyaka wajen yabona, kamar yadda Nasara suka wuce iyaka wajen yabon dan Maryam, ni kawai bawan Allah ne, sai ku ce bawan Allah kuma manzonsa". [Bukhari#3445].

6. Bai yarda wani ya mike masa tsaye ko ya tsaya a bayansa yana zaune da sunan girmamawa ba. Duk sanda ya zo majalisa, to yakan zauna inda duk ya sami wurin zama. Idan yana cikin sahabbansa kuwa yakan saje da su har bako idan ya zo ba ya iya tantance shi a tsakaninsu.

7. Wannan digo ne daga tekun kyawawan halayen Manzon Allah (SAW) da saukin kansa, wadanda da su ne ya gagari duk makiyansa, da kuma su ne ya mamaye zukatan mabiyansa, har suka so shi suka kuma kaunace shi fiye da komai a rayuwarsu.

8. Mu kwatanta wasu daga cikin kyawawan halayensa a rayuwarmu, don mu ga irin girman tasirin da za su yi mana wajen samun nasara a komai na rayuwarmu.

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...