Dr. Muhd Sani Umar R/lemo
Ramadaniyyat (1440H) [16]
*Mafi Munin Butulci*
Allah Ta'ala yana cewa :-
1. (Shin ba ka ga wadanda suka musanya ni’imar Allah da kafirci ba, suka kuma jefa mutanensu gidan hallaka?) [Suratu Ibrahim, aya ta 28].
2. Babu shakka duk wanda ya karanta tarihin duniya tun kafuwarta zuwa yau zai tabbatar da cewa, Allah bai yi wa dan’adam wata gagarumar ni’ima wadda ta kai aiko da manzanni ga mutane ba.
3. Don haka babu wadanda suka cika butulu kamar wadanda suka bijire wa annabawa suka kuma karyata su.
4. Mafi girman ni’ima cikin dangogin wannan ni’imar ita ce ni’imar aiko da Manzon Allah Muhammadu (SAW), don haka babu mafi munin butulci kamar kafirce masa da watsi da karantarwarsa
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment