Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Ramadaniyyat (1440H): *[13]*

*Yada Alfasha A Cikin Al'umma*

1. Allah (SAW) ya ce:
(Lalle wadanda suke son yaduwar mummunan abu game da wadanda suka yi imani suna da (sakamakon) azaba mai radadi a duniya da lahira, kuma Allah (Shi) Yake da masaniya, ku kuma ba abin da kuka sani) [Suratun Nur, aya ta 19].

2. Wannan ayar ta kunshi bayanin haramcin yada barna a cikin muminai ko da kuwa ta hanyar baza labarinta ne, domin yin haka zai taimaka wajen tallata ta a zukatan masu raunin imani da lalata kyakkyawar zamantakewar al'umma da gurbata tarbiyyarsu.

3. Mai kuzuzuta labarin wasu miyagu halaye na jama'a ya fi laifi a wurin Allah fiye da wanda zai aikata su a boye, domin mai aikata laifi a boye yana yin abin da kansa kadai zai cutar ba zai cutar da wani ba. Amma wanda yake kuzuzuta labarin miyagun dabi'u cikin al'umma wannan laifi ne da zai cutar da dukkan daukacin al'umma, ba kawai zai takaita a kansa shi kadai ba ne.

4. Yada labarin mummunan abu da ke faruwa a cikin al'umma da terere da masu aikata shi haramun ne a Shari'a. Ya kuma zama haramun ne ba don yana labarin karya ba, a'a sai domin mummunan tasirin da yake yi na wargaje zamantakewa da rusa katangar kunya a cikin al'umma.

5. Babban malamin nan tabi'i Ada'u dan Rabah yana cewa: (Duk mai yayata alfasha, to ya cancanci mummun horo ko da kuwa gaskiya yake fadi). [Dubi, Ibn Abi Hatim, Tafsirinsa Juzu'i na 8, shafi 2550].

6. Wanda duk yake yada labaran miyagun laifuffukan da wasu suka aikata ko da kuwa ba ya kama sunan kowa, to yana aikin ruguza al'umma ne, domin kuwa yana koya wa masu karancin tarbiyya wannan laifin ne, yana kuma tunatar da wadanda suka manta da shi, sannan yana zaburar da wadanda suke fargabar aikatawa domin ya nuna musu cewa a kalla wannan laifin mai yiwu wa ne ga duk wanda ya sa kansa, domin ga misali a fili.

7. Wajibi ne a kan masu magana a kafofin watsa labarai (Rediyo da Talabijin da Yanar gizo-gizo) su guji wannan mummunan hali, su daina yada labaran ababan kunya da alfasha a cikin al'umma, musamman yayin da wasu suke gaban kutuna ana shari'arsu, idan kuwa sun ki, to su sani mummunan sakamakon da Allah ya ambata yana nan yana jiran su. Allah ya kiyaye mana imaninmu. Amin.

8. An karbo daga Sauban (RA) ya ce: Annabi (SAW) ya ce: “Kada ku cutar da bayin Allah, kada kuma ku kunyata su, kada ku bibiyi al’aurarsu, domin duk wanda ya bibiyi al’aurar dan’uwansa Musulmi, to shi ma Allah zai bibiyi al’aurarsa har cikin gidansa ya kunyata shi.” [Ahmad #22402].

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...