Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Ramadaniyyat (1440H) *[24]*

*Kashe-Kashen* *Abokan Hulda*
*Abokan hulda kashi hudu ne*

*1. Na farko, wadanda kake bukatar hulda da su a koyaushe, dare ne ko rana, kamar yadda kake da bukatar ci da sha. Babu ranar da za ka daina bukatarsu a rayuwarka. Wadannan su ne malamai na Allah, wadanda suka san umarni da hani na Ubangiji, suka san hanyoyin makircin Shaidan ga dan'adam, suka kuma san cututtukan zukata da magungunansu. Su ne masu yin nasiha don Allah a bisa littafin Allah da sunnar Manzon Allah (SAW).*
*
2. Kashi na biyu, su ne wadanda hulda da su take kamar hulda da magani da za ka bukata yayin da kake rashin lafiya, da zarar ka samu lafiya sai ka dakatar da hulda da shi. Wadannan su ne wadanda kake kulla huldar rayuwar duniya ita kadai da su. Duk sanda bukatarka a wajensu ta kare sai kowa ya kama gabansa.*

*3. Kashi na uku, su ne wandanda hulda da su ta zamo maka kamar wata cuta mai wuyar magani. Su ne wadanda ba za ka ci ribar duniya ballantana ta lahira a wajensu ba. A madadin haka ma sai dai su jawo maka asarar duniya ko ta lahira ko duka biyun. To duk wanda ya rungumi hulda da irin wadannan to ya sani zai kashe kansa ne murus.*

*4. Daga cikin wannan kashi akwai wanda hulda da shi kamar ciwon hakori ne mai tsanani, amma da zarar an cire shi sai mutum ya sami lafiya. Akwai kuma wanda hulda da shi take kamar zazzabi mai zafi. Shi ne mutumin da yake da rangwamen hankali, wanda bai iya magana ba ballanta ka amfana da maganganunsa, sannan bai san ya yi shiru ya saurare ka ba ballantana ya karu da maganarka. Idan yana magana sai ya rika jiji da kai yana zaton maganarsa tana birge masu sauraronsa. Amma da ya yi shiru sai kowa ya ji kamar an sauke masa wani kaya ne mai nauyi daga kansa. Idan Allah ya so jarrabar bawansa sai ya hada shi zama da irin wannan mutum, hulda da shi ta zamo masa dole. Duk wanda Allah ya jarrabe shi da haka, to ya yi kokari ya kyautata mu'amalarsa gare shi har zuwa lokacin da Allah zai kawo masa mafita, ya raba su.*

*5. Kashi na hudu, shi ne wanda hulda da shi take tamkar dafi ko guba mai hallakarwa. Idan mutum ya sake ya sha ta, to hallaka ce a gabansa babu makawa. Idan an yi dace an samu makarin wannan dafin, sai ya tsira da rayuwarsa, idan kuwa ba a sami makarinsa ba, to sai dai a shirya jana'izarsa. Wadannan su ne masu gurbataccen addini masu kokarin hallaka bawa da ingiza shi cikin sabon Allah da Manzonsa da rungumar hanyar bidi'a da bata da son zuciya. Allah ya mana tsari. Amin.*
[Dubi, Ibnul Kayyim, Bada'i'ul Fawa'id, juzu'i na 2, shafi na 273-274].

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...