*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadiniyyat (1440H) *[25]*
*Kishin Kasa*
Allah yana cewa:
(Kuma in da a ce lalle mun wajabta musu cewa: “Ku kashe kawunanku ko ku fita daga gidajenku,” da ‘yan kadan ne daga cikinsu za su aikata hakan.) [Suratun Nisa'i, aya ta 66].
1. A wannan ayar Allah Ta'ala ya nuna yadda ya dasa wa dan'adam son kasar haihuwarsa, har ma ya nuna cewa fitar da shi daga mahaifarsa daidai yake da raba shi da rayuwarsa.
2. Babu shakka yayin da aka haifi mutum ya bude idon ya ga 'yan'uwansa da ke kewaye da shi a gidansu, ya kula da kaunar da suke nuna masa da kulawar da suke ba shi, ba shakka wannan zai dasa masa son gidansu da kishinsa a zuciyarsa. Yayin da yi yi wayo har ya fara shiga jama'ar unguwarsa, ya rika cudanya da su, har ya kai ga gane amafaninsu a gare shi, ya kuma fahimci cewa sun yi tarayya da shi a cikin abubuwa da dama, wasu ma sun hada dangantaka ta jini da haihuwa da shi, to babu shakka wannan kuma zai dasa masa son unguwarsa da kishin jama'arsa.
3. Yayin da kuma ya kai munzalin babban mutum ya shiga mu'amala da 'yan kasarsa masu yare da al'adu irin nasa, ya fuskanci cewa su ma suna da dabi'u da bukatu iri daya da nasa, to daga nan ne son kasarsa da kishin al'ummarsa zai dasu a cikin zuciyarsa. Don haka duk inda ya je zai yi ta marmarin ya dawo kasarsa ta haihuwa. A kuma duk inda yake a kasarsa zai yi ta begen unguwarsu da gidan da aka yanke masa cibiya. Baba mai ja da wannan sai wanda zai yi inkarin fidira ta halitta da Allah ya wa dan'adam.
4. Duk da haka mutane sun kasu kashi hudu dangane da son gidajensu ko jama'arsu ko kishin kasashensu:
5. Kashi na farko, su ne masu nuna da son kai, wadanda ba sa tunanin taimakon kowa sai iyalansu da mutanen gidansu. Batun mahaifarsu ko kasarsu ba ya gabansu samsam. Ko da sun shiga cikin jama'ar unguwa ko ta kasa, to suna zama da su ne a matsayin 'kaska rabi mai jini'. Sau tari irin wadannan mutane ba su da wani amfani har ma ga iyalan nasu da 'yan'uwansu domin tsananin son kansu.
6. Kashi na biyu, su ne wadanda ba su manta da mahaifarsu ba, suna kishinta matuka suna kuma kokarin su ga sun amfanar da jama'ar yankinsu. Amma wajen nuna nasu kishin sukan bi kowace irin hanya halattaciya da haramtacciya, ko da kuwa ta hanyar su cutar da wasu jama'ar ne. Sukan yi kokarin tsotsar jinin wasu al'ummu da danne su da nuna musu wulakanci da tauye hakkokinsu domin su dadada wa nasu. To irin wadannan mutane annuba ne ga sauran al'ummu kai har ma ga tasu jama'ar, domin ba abin da za su jawo musu sai bala'i da bakin jini.
7. Kashi na uku, su kuma su ne wadanda 'yancin kasarsu kawai suka sani, ba su yarda cewa wasu kasashe suna da 'yanci ba. Addininsu kadai shi ne mai gata, ba su yarda wasu masu wani addini ba su ma su sami gatan yin nasu addinin. Sukan yi fafutakar danne 'yancin wasu kasashe, wani lokacin ma ta hanyar mamaya da mulkin danniya, ba kuma za su kyale su ba ta ruwan sanyi sai dai ta tsiya. To irin wadannan suna karo da asalin abin da Allah ya dasa wa mutane ne na son kasarsu da mahallansu da danginsu.
8. Kashi na hudu, su ne wadanda suka yarda da cewa Allah ya dasa wa kowa son kasarsa a halittarsa ta farko da yi yi masa. Sannan suke mu'amala da kowa gwargwadon yadda jiren kaunarsu ya da dasu a zukatansu, wadda yana farawa ne daga gida sai mahalli sai kasa. Sukan ba kowa hakkinsa gwargwadon yadda ya dace ba tare da wani ya danne na wani ba. Wannan shi ne kishin kasa na gaskiya da Musulunci ya yarda da shi, ba kishi irin na dan tsako ba, ko na kwashe duka ba. Dubi Suratun Nisa'i aya ta 36].
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment