Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Ramadiniyyat (1440H) *[23]*

Rama Mugunta Da Alheri: *Darasi Daga Rayuwar Ibn Taimiyya*

1. Allah Ta'ala ya ce:
(Kyakkyawan (abu) da mummuna ba za su zama daya ba. To ka ture mummuna da abin da ya fi kyau, yayin nan sai ka ga wanda yake tsakaninsa da kai gaba ce ya zamanto kamar wani masoyi ne na kut da kut) [Fussilat, aya ta 34].

2. Imam Ibnul Kayyim yana magana a kan kyautata wa makiyi yayin da yake tsaka da rashin mutuncinsa, malam ya ce:
"Duk wanda yake son ya fahimci wannan babban matsayi, to ya karanta sirar Manzon Allah (SAW) da mu'amalarsa da mutane zai ga wannan dabi'a a fili. Babu wani wanda ya fi Manzon Allah siffantuwa da wannan kyakkywar dabi'a kamar Manzon Allah (SAW), sai kuma magadansa, kowanne gwargwadon kasonsa daga kayan gadonsa.
"Ban taba ganin mutumin da ya siffantu da wadannan kyawawan siffofi ba kamar Shaikhul Islam Ibn Taimiyya, Allah ya ji kansa. Wani daga cikin manyan abokansa yana cewa: 'Ina ma a ce zan iya kyautata wa abokaina kamar yadda Ibn Taimiyya yake kyautata wa makiyansa. Ban taba jinsa yana yi wa daya daga cikinsu mummunar addu'a ba, koyaushe sai dai na ji shi yana yi musu addu'o'i na alheri'.
"Wata rana na kawo masa albishir na mutuwar wani babban makiyinsa mai tsananin nuna masa gaba da cutarwa, amma sai ya daka mini tsawa, ya kama fadar 'Inna Lillahi Wa inna ilaihi raji'un'. Nan take ya tashi ya nufi gidan mamacin don yi wa iyalansa ta'aziyya, har ma ya rika fada musu cewa: 'Ni zan zama madadinsa a wurinku, kuma duk abin da kuke bukata na taimako zan yi muku'. Wannan ya yi matukar faranta musu rai, suka yi masa kyakkyawar addu'a, suka kuma girmama shi matuka".
[Dubi, Ibnul Kayyim, Madarijus Salikin, juzu'i na 2, shafi na 328-329].

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...