*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadaniyyat (1440H) *[2]*
Kaurace Wa Alkur'ani: Kashe-Kashensa Da Matakansu:
1. Allah (SWT) yana cewa:
(Manzo kuma ya ce: “Ya Ubangijina, lalle mutanena sun riki wannan Alkur’ani abin kaurace wa.”).
2. A wannan ayar Allah (SWT) ya bayyana yadda Manzon Allah (SAW) yake ta kokawa game da halayyar kafirai wadanda suke bijire wa Alkur’ani da ya zo yana karanta musu suka rika yi masa izgili da ta’annuti iri-iri, duk da cewa wajibi ne a kansu su yi imani da shi su mika wuya a gare shi.
Akwai matakai guda hudu na kaurace wa Alkur'ani:
Na farko, shi ne bijire masa da kafirce masa, kamar yadda kafirai suka rika nuna wa lokacin da Manzon Allah (SAW) yake karanta musu ayoyisa, har suka rika yi masa izgili suna sifanta shi da munanan siffofi don su sa mutane su guje shi, suka rika cewa tsafi ne ko waka ce ko su ce bokanci ne da dabo.
Na biyu, kaurace wa karatunsa da tilawarsa. Wajibi ne a kan kowane Musulmi ya zamanto mai karanta Alkur'ani lokaci bayan lokaci tare da kokarin haddace abin da ya sauwaka daga cikinsa ayoyinsa. Zunubi ne babba ga Musulmi ya yi watsi da karatun Alkura'ni gaba daya saboda bijirewa. Kamar yadda yawancin malamai suka bayyana cewa sakaci wajen barin karatunsa shi ma laifi ne koda kuwa babu bijire wa a ciki.
Na uku, kaurace wa tuntuntuni game da ma'anoninsa da kokarin fahimtar hukunce-hukuncesa. Domin babbar manufar da ta sa Allah ya saukar da shi ita ce saboda a fahimci ma'anoninsa a yi aiki da karantarwarsa. Don haka masu kiraye-kirayen cewa a daina taimaka wa wajen yada tafsirin Alkur'ani a kafofi watsa labarai a cikin wannan wata mai alfarma na Ramadan suna kira ne zuwa ga kaurace wa fahimatar da mutane karantarwar Alkur'ani da kusanto musu da ma'anoninsa domin aiki da shi.
Na hudu, kaurace wa aiki da hukunce-hukuncesa da watsi da shari'arsa da rashin zartar da umarninsa da haninsa. Kamar yadda wasu shugabannin Musulmi suke yakar kafa shari'ar Musuluci cikin al'umma suke nuna gabarsu a fili game da duk wani yunkuri na tabbatar da haka. Wannan shi ma nau'i ne na kaurace wa Alkur'ani wanda Allah ya ba mu labarin cewa Mazonsa ya koka game da faruwarsa a cikin al'ummarsa.
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment