*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramdaniyyat (1440H)
*[1]*
Alakar Alkur'ani Da Watan Ramadan
1. Saukar da Alkur'ani a cikin watan Alkur'ani har sau biyu, watau saukarwa ta farko zuwa saman duniya ta kusa a Baitul Izza da sauka ta biyu zuwa ga Annabi SAW yayin da yake kebanta da kansa a kogon Hira, wannan duka yana nuna kakkarfar alakar dake tsakanin wannan wata mai albarka da Alkur'ani mai girma.
2. Manzon Allah (SAW) ya kasance yakan hadu da Mala'ika Jibrilu a duk shekara a watan Ramadana suna bitar Alkur'ani. A shekararsa ta karshe a duniya sun hadu sau biyu sun yi bitar Alkur'ani. Wannan yana kara tabbatar da kakkarfar alakar wannan watan da wannan babban littafin watau Alkur'ani.
3. Annabi (SAW) ya kwadaitar da al'ummarsa a kan tsayuwar dare don raya kwanakin wannan wata mai alfarma, ya yi musu albishir din gafarar zunubansu da suka gabata idan su aikata haka. Ya zamanto yana kara kaimi wajen ibadarsa da tsayuwarsa ta dare, yana tashin iyalansa daga barchi don su yi koyi da shi yayin da goman karshe ta shiga ta wannan watan. Duk wannan wani babban dalili ne mai tabbatar da karfin alakar watan Ramadan da wannan muhimmin littafin a rayuwar Musulmi watau Alkur'ani.
4. Musulmi a ko'ina a fadin duniya suna tashi tsaye don karfafa dangantakarsu da wannan littafi ta wajen karanta shi da karantar da shi da tuntuntuni cikin ayoyinsa ya yada koyarwarsa a birni da kauye ta hanyoyi daban-daban wadanda suka hada da karantar da shi a masallatai da majalisan ilimi da makarantu da daukar nayin yada karatunsa da tafsirinsa a kafofin sadawarwa daban-daban wadanda suka hada da Radiyo da Talabijin da hanyoyin sadawarwa na yanar gizo-gizo (internet) da sauransu.
5. Madalla da duk wanda ya tsinci kansa cikin wannan aiki na alheri da raya sunnar Mazon Allah (SAW). Allah muke fata ya karbi ayyukanmu nagari ya yafe mana kurakuranmu ya sanya mu cikin 'yantattu a wannan watan. Amin.
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment