*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadaniyyat (1440H) *[27]*
*Hudubar Usman Bin Affan* Ta Karshe
A karshen rayuwarsa sayyiduna Usman dan Affan (RA) ya yi wa jama'a hudubar karshe inda yake cewa da su:
1. "Lalle Allah (SAW) ya ba ku duniya ne domin ku nemi lahira da ita. Bai ba ku ita ba don ku raja'a a kanta.
2. "Duniya mai karewa ce, lahira ce kadai mai wanzuwa har abada. Kada ku bari mai karewa (duniya) ta sanya muku girman kai. Kada kuma ku yarda ta dauke muku hankali har ku manta da mai wanzuwa (lahira).
3."Ku fifita abin da zai dawwama har abada a kan wanda zai kare, domin duniya mai yankewa ce, kuma zuwa ga Allah ne makoma take.
4. "Ku kiyaye dokokin Allah, domin ta haka ne za ku sanya shamaki tsakaninku da azabarsa, sannan ku sami tsanin da zai kai ku zuwa gare shi.
5. Ku kiyayi kishin Allah, ku kuma ci gaba da zama kanku a hade, kada ku rarrabu kungiya-kungiya: (Ku tuna ni'imar Allah da ya yi muku yayin da kuka zamo abokan gaban juna sai ya hada tsakanin zukatanku, sai kuka zamo 'yan’uwan juna a sakamakon ni'imarsa.)".
[Dubi, Ibn Asaakir, Taarikhu Dimashk, juzi'i na 39, shafi na 238].
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment