*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadaniyyat (1440H) *[28]*
*Fiyayyar Al'umma A Bayan Kasa*
1. Allah Ta'ala yana cewa:
(Ku ne mafi alherin al'umma wadanda aka fitar ga mutane, kuna umarni da kyakkyawan aiki, kuma kuna hana mummuna aiki, kuma kuna yin imani da Allah) [Ali Imaran, 110]
2. Ya kamata al’ummar Musulmi su fahimci cewa, su ne fiyayyu a cikin duk wata al’umma da aka taba yi a bayan kasa, don su fahimci kimarsu da darajarsu, kuma su gane cewa, sun fito ne don su ja ragamar tafiyar sauran al'ummu. Kuma nufin Allah shi ne alheri ya yi jagoranci a bayan kasa ba sharri ba, a bayan kasa, don haka ya kamata su zama koyaushe su ne masu bayarwa, ba masu karba ba. Kuma abin da za su bayar na akida da ilimi da halayya da tsarin rayuwa ya zama mai inganci ne.
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment