Ads

Monday, 3 June 2019

*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*

Ramadaniyyat (1440H) *[11]*

*Sukan Malaman Sunna: Hassada Ga Mai Rabo Taki Ce*

1. Sukan malamai magada annabawa masu karantar da mutane addinin Allah wani mugun abu ne da ya dade a cikin al'umma, kuma salo ne na wasu masu miyagun akidu da bidi'o'i da suke da damuwa game da rawar da malamai suke takawa wajen bayyana wa mutanen munin akidunsu. Hakanan mutane masu dauke da cutar hassada a zukatansu sukan damu da ganin karbuwa da wani malami ya samu a wurin al'umma da tasirin da kalmarsa take da shi a tsakaninsu, don haka suke ganin cewa su fa zakaransu ba zai taba yin cara ba har sai ta hanyar sukan malamai da tuhumarsu da yi musu karerayi.

2. Daga cikin labaran da tarihi ya tabbatar mana na irin wadannan mutane akwai abin da ya faru da babban malamin sunnar nan, wato Abu Umar Ahmad bn Muhammad at-Talamanki Al-Maliki (ya rasu shekara ta 429H).

3. Ya kasance babban malami ne masanin Alkur'ani da hadisi da ilimin fikihu. Ya yi rubuce-rubuce da dama a fannonin ilimi masu yawa. Ya yi sanadiyyar shigar da ilimi mai yawa cikin yankin kasar Andalus, kuma mutum ne mai matukar kishin Shari'a da Sunna.

4. A shekara ta 425 ne aka samu wasu gungun 'malamai' wadanda suka shirya taro a gidan daya daga cikinsu, inda suka zauna suka rubuta tuhumar karya a kansa cewa, wai yana da akidar 'Khawarijawa' watau akidar masu fito-na-fito da masu mulki ta hanyar amfani da karfi da kuma kafirta musulmi masu aikata kaba'ira.

5. Wannan tuhuma ita ce ta sa har aka gurfanar da Imam Abu Umar gaban Alkali Muhammad Fartun, aka kuma samu mutane goma sha biyar wadanda suka ba da shaidar zur a kan tabbatar da wannan tuhuma da ake yi masa. To amma daga bisani bayan alkali ya yi bincike sai ya gane cewa wannan tuhumar da ake yi Imam Abu Umar tuhumar banza ce babu kanshin gaskiya ko kadan a cikinta, don haka sai ya sallame shi, ya kuma rubuta masa takardar wanke shi daga wannan zargi ya danka masa a hannunsa.

6. Tun daga lokacin Allah ya ci gaba da daukaka sunan wannan malami, ya kuma ci gaba da raya iliminsa cikin al'umma tsawon zamani har zuwa yau kimanin shekara dubu ke nan. Su kuma wadanda suka so rusa shi sai Allah ya rusa kadararsu, a yau ba wanda aka san ko da sunansa daga cikinsu ballanta a ambaci alherinsa a yi masa kyakkyawar addu'a. Ashe yanzu wannan bai isa izina ba?
[Dubi, Ibnul Abbar, At-Takmilah, juzu'i na 1 shafi na273, da Az-Zahabi, Siyarun Nubala' juzu'i na 17, shafi na 568].

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...