Ads

Monday, 10 June 2019

Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Sokoto

****Gaskiya zuma ce. Akwai harbi amma tana da zaqi. Wanda aka buge shi da bulalar gaskiya bai fadi ba, ka sa masa ido, idan ya karasa gaba zai fadi.

****Ana ba da baya wani lokaci ba don tsoro ko jin girman kai ba. Sai don kauce ma karo da wanda bai dace ba. 

****Mai hankali idan ya yi magana sai ya kawo hujja. Wawa idan ya yi magana sai ya yi ta rantsuwa. Mai gaskiya ba ya buqatar rantse rantse. Gaskiya ba ta neman ado.

****Ana samun Rayuwa mai dadi ta hanyar barin wasu abubuwa fiye da yadda ake samun ta ta hanyar samun wasu.

****Wanda yake ba da turare ba za a rasa kamshi a hannunsa ba. Mai yin alheri ba zai rasa samun alheri ba

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...