Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Sokoto
****Gaskiya zuma ce. Akwai harbi amma tana da zaqi. Wanda aka buge shi da bulalar gaskiya bai fadi ba, ka sa masa ido, idan ya karasa gaba zai fadi.
****Ana ba da baya wani lokaci ba don tsoro ko jin girman kai ba. Sai don kauce ma karo da wanda bai dace ba.
****Mai hankali idan ya yi magana sai ya kawo hujja. Wawa idan ya yi magana sai ya yi ta rantsuwa. Mai gaskiya ba ya buqatar rantse rantse. Gaskiya ba ta neman ado.
****Ana samun Rayuwa mai dadi ta hanyar barin wasu abubuwa fiye da yadda ake samun ta ta hanyar samun wasu.
****Wanda yake ba da turare ba za a rasa kamshi a hannunsa ba. Mai yin alheri ba zai rasa samun alheri ba
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 10 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment