Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Sokoto
****Idan za ka aiki dan saqo kada ka aiki wawa. Nemi mai hankali da basira. Idan har ba ka samu ba, to ka je da kanka.
****Idan za ka aiki dan saqo kada ka aiki wawa. Nemi mai hankali da basira. Idan har ba ka samu ba, to ka je da kanka.
****Idan mutane suka guje ka a lokacin da ka shiga jarrabawar rayuwa to ka kwantar da hankalinka. Allah bai kore maka su ba sai don yana son ya ishe ka.
****Kada ka damu idan ka yi kuskure sannan ka gyara. Daga kurakuranka ne kake karanta rayuwar duniya.
****Idan ka samu alheri, yi godiya. Idan sharri ya same ka, yi haquri. Idan ni'ima ta girma ya kamata godiyarta ta girma.
****Motsin da ya fi kowane sauqi gare ka shi ne motsa harshenka. Amma kuma ya fi kowane hatsari da cutarwa a gare ka idan ba ka kiyaye shi ba.
No comments:
Post a Comment