Ads

Wednesday, 5 June 2019

DUNIYAN MAKARANTA


Rubutawa: Dr. Muhammad Mansur Sokoto

****Idan za ka aiki dan saqo kada ka aiki wawa. Nemi mai hankali da basira. Idan har ba ka samu ba, to ka je da kanka.

****Idan mutane suka guje ka a lokacin da ka shiga jarrabawar rayuwa to ka kwantar da hankalinka. Allah bai kore maka su ba sai don yana son ya ishe ka.

****Kada ka damu idan ka yi kuskure sannan ka gyara. Daga kurakuranka ne kake karanta rayuwar duniya. 
****Idan ka samu alheri, yi godiya. Idan sharri ya same ka, yi haquri. Idan ni'ima ta girma ya kamata godiyarta ta girma.

****Motsin da ya fi kowane sauqi gare ka shi ne motsa harshenka. Amma kuma ya fi kowane hatsari da cutarwa a gare ka idan ba ka kiyaye shi ba.

No comments:

Post a Comment

FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...