*Dr. Muhd Sani Umar R/lemo*
Ramadaniyyat (1440H) *[9]*
*Hikimar Imani Da Kaddara*
1. Ibnul Jauzi ya ba da labari cewa: Wata rana wani mutum ya fadi ya suma, sai mutane suka zaci cewa rai ya yi halinsa. Sai nan da nan aka nemo mai wankan gawa, aka dora shi a kan abin wanka. Zuba wa mutumin nan ruwan sanyi ke da wuya sai ya yi zumbur ya tashi tsaye, daga nan sai shi kuma mai wankan gawa ya firgita saboda tsananin tsoro ya fadi ya mutu nan take.
2. Wannan yana tabbatar da cewa komai kaddara ce. Don haka ka ci gaba da kokarinka a kan gaskiya da jajirce mata, kada tsoron mutuwa ya hana ka riko da ita da tsayawa a kanta. Ajalin kowa a lissafe yake a wurin Allah. Zakaran da Allah ya nufa da cara ko ana muzuru ana shaho sai ya yi.
3. Ka yi aikinka domin rayuwarka ta duniya kamar ba za ka mutu ba har abada, ka kuma nemi lahirarka kamar gobe ne ranar mutuwarka.
4. Imani da kaddara shi ne rayuwa, shi ne zai zamo maka haske yayin da ka shiga cikin duhu. Da shi ne za ka rika hango mafita yayin da kake fuskantar wani tsanani.
5. Imani da kaddara shi ne abin da yake kwantar wa da bawa hankali, ya dawo masa da nutsuwarsa cikin kankanin lokaci. Idan ka rasa da daya, to ka dubi wani shi 'ya'ya biyu ya rasa, sai ka gode wa Allah. Idan ka yi asarar dubu daya, to ka dubi wanda ya yi hasarar dubu biyu, sai ka gode wa Allah. Da wannan ne za ka fahimci sirrin imani da kaddara.
6. Don haka mu aikata aikin alheri tukuru, kada mu samu damuwa don mun kasa cin nasarar abin da muka sa a gaba. Kada kuma mu fitar da kauna don mun ga tafiyarmu tana kara tsawo ba tare da mun cimma inda muka nufa ba.
7. Mu kasance tare da 'Kaddara' koyaushe kamar mutumin da ya zo tsallaka hanya mai cike da zurga-zurgar ababan hawa, idan zai rika tuna hatsurran ababan hawa, to har abada ba zai tsallaka wannan hanya ba. Hakanan idan zuciyarsa ta fada masa cewa zai iya tunkarar wadannan ababan hawa ya ture su wuri guda ya wuce abinsa, to ba zai kai labari ba. Amma idan ya nutsu ya ketare hanyarsa cikin taka-tsantsan, to wannan shi ne mai hankali. Sannan idan ya ketare lafiya sai ya yi wa Allah godiya, idan kuma wani abin ki ne ya faru da shi, to zai tuna cewa ba sakacinsa ba ne, hukunci ne kawai na kaddara. Allah yana cewa: (Lalle Mu Mun halicci komai da kaddara). [Suratul Kamar, aya ta 49].
Dubi, Ali At-Tantawi, Suwarun Wa Khawatir, shafi na 125-126.
Wannan website mun bude shi ne dan watsa duk abinda muka san insha Allahu zai anfani al'umma.
Ads
Monday, 3 June 2019
Subscribe to:
Post Comments (Atom)
FA'IDODIN ALBASA ************************ Da Sunan Allah mai sadar da rahama zuwa ga bayinsa, Salati da aminci su tabbata bisa Fiyayye...
-
Hadisi daga Hasanul Basariy daga Sayyiduna Anas bn Malik (ra) yace: “Akwai wani mutum daga cikin Sahabban Manzon Allah (saww) daga cikin...
-
****Babu Abin da yake tabbas a duniya sai Canji. Komai ka gani a yau watarana zai canja daga yadda ka san shi. Komai yana canjawa ban da sar...
-
Lokacin da Shehu Jaha yana alkalanci a birnin Aku Shahar, sai ga wasu mutane sun zo gabansa suna rikici kamar sa naushi juna. Da suka gurfan...
No comments:
Post a Comment